1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan: Dambarwar rikicin juyin mulki

Abdullahi Tanko Bala
October 28, 2021

Jami'an tsaro sun yi arangama da masu zanga zanga wadanda suka fusata da juyin mulkin da sojoji suka yi wanda ya kassara shirin gwamnatin wucin gadi na mayar da kasar kan tafarkin dmikuradiyya.

https://p.dw.com/p/42Jkv
Sudan Putsch Protest Ausschreitungen
Hoto: AFP/Getty Images

Juyin mulkin na Sudan ya janyo martani na kasashen duniya wadanda suka bukaci sojojin su mayar da kasar tafarki.

Kwamintin sulhun Majalisar Dinkin Duniya da shugaban Amirka Joe Biden sun yi kira a gaggauta mayar da gwamnatin farar hula da sojojin suka hambarar.

Duka mambobin kwamitin sulhun sun baiyana matukar damuwa da juyin mulkin wanda ya mayar da kasar baya.

Janar Abdel-Fattah al-Burhan wanda ya jagoranci juyin mulkin da ya hambarar da tsohon shugaba Omar al-Bashir bayan zanga zangar gama gari ta matasa ya rusa gwamnatin kasar da ke tangal tangal.