1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Halitta da MuhalliMaroko

Maroko: Ana ci gaba da aikin ceto bayan girgizar kasa

September 10, 2023

Kasar Maroko ta sanar da soke dukkanin taruka a kasar, bayan girgizar kasa mafi muni cikin shekaru 120 a yankin, a daidai lokacin da kasashen duniya ke ci gaba da kai dauki don ceto wadanda iftila'in ya ritsa da su

https://p.dw.com/p/4W8ac
Masu aikin ceto bayan aukuwar girgizar kasa a Maroko
Masu aikin ceto bayan aukuwar girgizar kasa a MarokoHoto: Fadel Senna/AFP/Getty Images

Girgizar kasa mai karfin gaske ta auku a kasar Maroko, inda kawo yanzu ta yi ajalin mutane sama da 2000. Ma'aikatar kula da harkokin cikin gida ta kasar ta ce iftila'in ya faru ne a ranar Juma'a da daddare, ta kuma ce ta yi nasarar ceto rayukan mutum sama da 2000 da tuni aka kwantar da su a cibiyoyin kiwon lafiya.

Daruruwan mutane sun mutu a girgizar kasa a Maroko
Daruruwan mutane sun mutu a girgizar kasa a MarokoHoto: Fadel Senna/AFP/Getty Images

Masana sun ce karfin girgizar kasar ya kai zurfin kilomita 18.5 a karkashin kasa. Cikin biranen da abin ya faru akwai  al-Haouz da Marrakesh da Azilal da sauransu. Wannan dai ita ce girgizar kasa da a karon farko karfinta ya girgiza hatta biranen Rabat da Casablanca da ke makwabtaka da biranen da ta fi kamari.

Maroko | Daruruwan mutane sun mutu a girgizar kasa
Maroko | Daruruwan mutane sun mutu a girgizar kasaHoto: Saouri Aissa/Xinhua/IMAGO

Gidaje da yawa sun ruguje, lamarin da ya yi sanadiyyar katsewar wutar lantarki a sassa dabam-daban. Sai dai mahukuntan kasar sun ce girgizar kasar ta fi muni a yankunan karkara da ke nesa da manyan birane.

Shugabannin duniya musamman wadanda ke halartar taron koli na kungiyar kasashe 20 masu karfin tattalin arziki, G20, sun aike wa Sarki Mohammed VI ( na 6) sakon jaje da ta'aziyyarsu ga gwamnatin Maroko a kan wannan al'amari, inda wasu daga cikin shugabannin suka fara kokarin ganin yadda za aike wa da Marokon gudunmawar tallafa wa mutanen kasar gina sabuwar rayuwa.