1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dubban Falasdinawa sun rasa rayukansu

Binta Aliyu Zurmi
October 28, 2023

Ma'aikatar lafiya ta Falasdinu ta ce adadin wadanda suka rasa rayukansu tun bayan kaddamar da yaki da Isra'ila ta yi,ya zuwa yanzu ya kai sama da mutum dubu 7,700.

https://p.dw.com/p/4Y9Kz
Israel | Rauch steigt auf | Zerstörungen nach Bombeneinschlag
Hoto: Ohad Zwigenberg/AP Photo/picture alliance

A cewar sanarwar da hukumomin Gaza, sama da dubu 3,500 kananan yara ne.

A daren jiya ne Isra'ila ta kaddamar da wani sabon hari ta sama da kasa a Gaza, inda rahotanni suka ce sama da jiragen yaki 100 ne suka yi luguden wuta a wani yunkuri na kakkabe mayakan Hamas. An dai katse hanyoyin sadarwa a illahirin yankin da ma wutar lantarki.

Kakain rundunar sojin Isra'ila, Daniel Hagari, ya ce kutsen ta kasa, munafarsa shi ne kame wasu yankuna a arewacin Zirin da kuma ragargaza wasu runbunan makamai da tungogin mayakan Hamas.

 

Karin bayani:  Sojojin Isra'ila sun kutsa Zirin Gaza ta kasa

 

Dubban gidaje ne wannan sabon harin ya lalata inji hukumomin Hamas.

Harin na zama mafi muni da ba a ga irinsa ba kwanaki 21 tun bayan barkewarsa.

Shugaba Recep Tayyip Erdogang na Turkiyya ya kira wannan sabon harin na Isra'ila a Gaza da na rashin hankali da imani, ya kuma nemi 'yan kasar da su fito tattakin nuna goyon baya ga al'ummar Falasdinu.