1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Cece- kuce a jam'iyyar PDP bayan da ta sha kaye

Ubale Musa daga AbujaApril 30, 2015

Shugaban PDP Ahmad Adamu Mu'azu ya ki halartar waiwayen da jam'iyyar ta yi a kan musababbin shan kaye a zabukan da suka gudana, saboda barazanar tsigewa da ya ke fuskanta.

https://p.dw.com/p/1FISL
Hoto: DW/U.Musa

Shugaban kasa Goodluck Jonathan ya karbi rahoton 'yan kwamitin yakin neman zabensa, a wani abun da ke zaman damar farko a tsakanin bangarorin PDP da har yanzu ke tunanin mafita ga makomar jam'iyyar. Sai dai kuma shi da ragowar manyan jiga- jigan jam'iyyar dai, ra'ayi ya zo kusan daya game da musabbabin asarar zaben da ke zaman irinsa na farko da kuma har ya zuwa yanzu ba su kai ga farfadowa a cikinta ba.

Sun yin intifakin cewa rikicin cikin gida da ma rashin hadin kan 'ya'yan PDP ne musabbabin da ya sa jam'iyyar asarar mukamai masu muhimanci ciki har da na shugaban kasa da kuma na gwamnoni a yayin zaben.

Nigeria Regierungspartei PDP
PDP na shirin zama jam'iyyar adawa a NajeriyaHoto: DW/K. Gänsler

Sai dai kuma an kai ga mika rahoton ba tare da kasancewar shugabannin jam'iyyar na kasa baki daya ba musamman ma Ahmad Adamu Mu'azu da ke zama shugaban PDP. Tuni dai aka fara hasashen cewa gwamnonin PDP na kokarin tureshi daga shugabancin djam'iyyar tare da maye gurbinsa da Senata Liel Imoke gwamnan jihar Cross Rivers da ke shirin barin gado.

To sai dai kuma a fadar senator Walid Jibrin da ke zaman sakataren kwamitin amintattun PDP lokacin da jam'iyyar take ciki ba shi bukatar sabuwar baraka a tsakanin 'ya'yanta