An sace dalibai a Najeriya
October 10, 2023Talla
Kakakin rundunar 'yan sandan Jihar Nasarawa Rahman Nansel ya tabbatar da aukuwar lamarin cikin wata sanarwa da ya bayyana wa manema labarai a garin Lafiya. Inda ya ce yan bindigar sun shiga unguwar dauke da manyan bindigogi, suka sace daliban uku mata daya namiji. Rundunar 'yan sandan Jihar Nasarawa dai ta tabbatar da cewar ta baza jami'anta zuwa wurare dabam-dabam da nufin gano inda 'yan bindigar suka shiga da daliban.