SiyasaAfirka
'Yan bindiga a jihar Filato sun kashe gomman mutane.
December 26, 2023Talla
Hare-hare ne da suka faro daga Bokkos da yammacin ranar Lahadi, suka shige cikin yankin Barikin Ladi, inda da farko aka bayar da labarin mutuwar mutum 113.
Akwai ma wasu sama da mutum 300 da maharan suka jikkata, mutanen da a halin yanzu aka kwantar a asibitocin yankin Bokkos.
Hukumomin yankin na Bokkos dai sun ce hare-haren sun shafi akalla kauyuka 20 da ke cikin kananan hukumomin biyu na Bokkos da kuma Barikin Ladi
Wani dan majalisar jiha Dickson Chollom, wanda ya nuna takaici da abin da ya faru, ya yi kiran jami'an tsaro da su dauki mataki na gaggawa.
Kungiyar kare hakkin bil Adama ta Amnesty International ta zargi gwamnatin Najeriya da rashin daukar matakan da za su kawo karshen kare-kashe da ake yi a yankunan karkara a jihar Filato.