1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a yi zabe a Najeriya a Fabrairu

February 6, 2015

Hukumar zaɓe dai ta sha alwashin ganin ta kai ga mafi yawan waɗanda suka cancanci kaɗa kuri'a dan ba su katinsu na zaɓe gabanin wannan rana ta sha huɗu ga watan nan na Fabrairu.

https://p.dw.com/p/1EWMe
Wahlen Nigeria Auszählung Stimmen Wahllokal
Hoto: dapd

Majalisar ƙasa ta Najeriya ta zartar da ƙudurin ci gaba da zaɓen ƙasar ba tare da an dage shi ba kamar yadda wasu ke kiraye-kirayen a yi.

Majalisar wacce ta ƙunshi manyan 'yan takara biyu a zaɓen da ke tafe da tsaffin shugabanni a Najeriya da gwamnnoni ta cimma wannan matsayar ne a ƙarshen wani taro da ta shafe yinin jiya Alhamis tana gudanarwa a fadar Aso Rock karkashin jagorancin shugaba Goodluck Jonathan.

Wasu daga cikin ƙananan jam'iyyu da mai ba da shawara ga shugaban ƙasa kan sha'anin tsaro dai a Najeriyar sun buƙaci da a dage wannan zaɓe ta yadda kowane dan ƙasar zai samu katin kaɗa ƙuri'a .

Mawallafi: Yusuf Bala
Edita: Abdourahamane Hassane