1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabon

Gabon: 'Yan adawa na ikirarin lashe zabe

September 1, 2023

Yayin da ake shirin rantsar da janar Brice Oligui Nguema a matsayin shugaban rikon kwaryar Gabon a ranar Litinin mai zuwa, jam'iyyun adawan kasar sun bukaci da a amince da nasarar da dan takararsu ya samu a zaben kasar.

https://p.dw.com/p/4Vqoj
Madugun adawan Gabon Albert Ondo Ossa
'Yan adawa a Gabon na neman a ba su mulkiHoto: Gerauds Wilfried Obangome/REUTERS

Jam'iyyun adawan na Gabon sun yi tsokaci a karon farko tun bayan juyin mulki kasar, inda suka yaba da matakin da sojojin suka dauka domin kare dimukuradiyya. Sai daga bisani sun kuma bukaci sojojin da su tabbatar da nasarar da dan takararsu Albert Ondo Ossa ya samu a zaben kasar da aka gudanar a rnanar Asabar (26.08.23) wanda ya bar baya da kura.

Karin bayani: Sojoji sun yi juyin mulki a Gabon

Wannan furici na jam'iyyun adawan na zuwa ne a daidai lokacin da sabon jagoran sojojin ya fara girka sabbin hukumomin mulkin rikon kwarya tare da daukar sabbin kudurori, ciki har da canja ranar bikin samun 'yancin kan kasar daga 17 ga watan Ogusta inda mayar da shi izuwa ranar 30 ga watan Agusta, wacce ta zo daidai da ranar da aka hambarar da shugaba Ali Bongo.