1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

WHO: Gargadi kan gurguncewar tsarin kiwon lafiya a Gaza

November 11, 2023

Shugaban hukumar lafiya ta duniya WHO ya yi gargadi kan gurguncewar tsarin kiwon lafiya a zirin Gaza tare da yin shailar cewa rabi daga cikin ma'aikatun kiwon lafiya 36 na yankin ba sa aiki kwata-kwata.

https://p.dw.com/p/4Ygw9
WHO: Gargadi kan gurguncewar tsarin kiwon lafiya a Gaza
WHO: Gargadi kan gurguncewar tsarin kiwon lafiya a GazaHoto: Abed Zagout/Anadolu/picture alliance

Tedros  Ghebreyesus ya yi wannan gargadi ne yayin da yake gabatar da rahoto a gaban kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya inda ya ce al'amarin da ke a zahiri a Gaza ya wuce misali.

Karin bayani: Hukumomi a Gaza sun ce wasu hare-haren Isra'ila sun fada kan asibitoci guda uku a juma'ar nan

A rahoton nasa, Tedros Ghebreyesus ya kara da cewa an kai wa asibitoci da dakunan shan magani a Gaza fiye da hare-hare 250, sannan kuma lunguna da sako na asibitocin zirin sun cika sun batse da wadanda suka jikkata baya ga cinkoson gawarwaki, sannan kuma yanayin aiki ba a magana in ji shi.  

Karin bayani: Asibitoci da dama sun rufe a Zirin Gaza

Shugaban hukumar lafiyar ta duniya ya kuma yi kira da a sauya fasalin kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya duba da yadda ya gaza magana da murya daya domin daukar matakin kawo karshen wannan munmunan al'amari da ke faruwa a dan karamin yankin na Falasdinu.

Karin bayani:  Shugaban Amurka Joe Biden ya ce babu yiwuwar tsagaita wuta a Gaza