1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Trump ya ce Amurka za ta mallaki Gaza

Binta Aliyu Zurmi
February 10, 2025

Shugaba Donald Trump ya ce yana na a kan matsayarsa ta ganin cewa Amurka ta sayi Gaza bayan ficewar Falasdinawa ko kuma an cire su daga Zirin.

https://p.dw.com/p/4qFo2
USA 2024 | Trump kündigt Gespräche mit Putin und Selenskyj zur Beendigung des Ukraine-Kriegs an
Hoto: Andrew Harnik/GDA/La Nacion/IMAGO

Trump ya kara da cewar wasu kasashen da ke yankin Gabas ta Tsakiya za a ba su wani sashe na Zirin domin sake gina shi.

A karon farko shugaban na Amurka zai gana da sarki Abdallah II na kasar Jordan wanda ya gayyace shi fadar White House.

Dama a baya Trump ya ce kasashen Jordan da Masar su kwashe Falasdinawa sai dai wata majiya daga fadar Sarki Abdullah ta ce basaraken ba zai amince da batun kwashe Falasdinawa daga mahaifarsu ba.

 

Karin Bayani: Martani kan barazanar Trump na kwace iko da Gaza