Amsoshi: 21.10.2023
October 23, 2023Talla
Argungu birni ne, da ke a Jihar Kebbi a Najeriya, a kan kogin Sakwato. A shekara ta 2007 Argungu an ƙiyasin cewar garin yana jama'a 47,064. Birnin shi ne wurin zama na masarautar Argungu, jiha ce ta gargajiya. Garin babbar cibiyar noma ce ga yankin, tare da muhimman kayan amfanin gona da suka hada da taba, da gyada da shinkafa da gero da alkama, da dawa. Birnin kuma yana karbar bakuncin bikin kamun kifi na duniya na shekara-shekara wanda aka dakatar har tsawon shekaru 11. Amma an sake gudanar da bikin kamun kifi na Argungu a shekara ta 2020.