1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amsoshi: 21.10.2023

Usman Shehu Usman AH
October 23, 2023

Argungu karamar hukuma ce da ke a cikin Jihar Kebbi, a arewa maso yamman Najeriya, Al'ummar yankin na yin bikin al'ada na kamun kifi a duk shekara.

https://p.dw.com/p/4XteZ
Hoto: Pius Utomi Ekpei/AFP/Getty Images

MMT_Hörerfragen 21+22.10.2023 - MP3-Stereo

Argungu birni ne, da ke a Jihar Kebbi a Najeriya, a kan kogin Sakwato. A shekara ta 2007 Argungu an ƙiyasin cewar garin yana jama'a 47,064. Birnin shi ne wurin zama na masarautar Argungu, jiha ce ta gargajiya. Garin babbar cibiyar noma ce ga yankin, tare da muhimman kayan amfanin gona da suka hada da taba, da gyada da shinkafa da gero da alkama, da dawa. Birnin kuma yana karbar bakuncin bikin kamun kifi na duniya na shekara-shekara wanda aka dakatar har tsawon shekaru 11. Amma an  sake gudanar da bikin kamun kifi na Argungu a shekara ta 2020.