1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu ta soke sabbin sarakunan Kano

Nasir Salisu Zango AH
November 21, 2019

Babbar kotun jihar ta zartas da hukuncin rushe dokar da ta kirkiri sabbin sarakunan yanka guda 4 a Kano wanda ya sa sarakunan yanka suka zama guda biyar a jihar.

https://p.dw.com/p/3TTKF
Nigeria - Emir von Kano - Muhammadu Sanusi II
Hoto: Getty Images/AFP/A. Abubakar

Galibi dai mutane da dama sun bayyana cewar siyasa da kuma rikicin da ke tsakanin gwamna Ganduje da sarkin Kano Sarki Muhammadu Sanusi na 2 wadannan abubuwan sun taka rawa wajen kirkirar wadannan sabbin masarautu wadanda za su yi goggaya da sarkin Kano. Kotun karkashin alkali Usman Na Abba ta ayyana cewar dokar da majalisar dokokin Jihar kano ta dauka wacce ta bai wa gwamnati damar raba  masarautar Kano zuwa masarautu biyar, haramatacciya ce domin ba a bi ka'idojin da suka dace ba wajen girka wannan doka.

Shin mi zai iya biyo bayan yanke hukuncin da kotu ta yi, gwamnatin  Jihar Kanon za ta martaba dokar

Yayin zartas da hukuncin alkalin  ya bayyana cewar dukkanin hanyoyin da majalisar ta bi wajen yin dokar ba su da tushe don haka ta rushe wnanan doka. To amma wane mataki gwamnati za ta dauka a kan wannan hukunci da ake ganin ya mayar musu da hannun agogo baya. .

Nigeria Ramadan
Hoto: picture-alliance/AP Photo/G. Osodi

 Barrister Ibrahim Muktar ya bayyana cewar za su dauki mataki amma ba za su bayyana matakin ba sai sun kammala tattaunawa da sauran lauyoyi. A karshen zaman kotun dai alkali Usman Na Abba ya bayyana cewar akwai dama ga wanda duk bai aminta da hukuncin ba, domin ya daukaka kara zuwa kotun daukaka kara da ke Kaduna.