A cikin shirin za a ji cewa a yayin da Najeriya ke ci gaba da fuskantar barazana a bangaren tsaro, a wannan Alhamis majalisar tsoffin shugabannin kasar sun gana da Shugaba Muhammadu Buhari. Ministar harkokin wajen Jamus Annalena Baerbock ta yi kira ga kasashen duniya da su kai wa wasu kasashen Afirka dauki musamman wadanda ke fuskntar matsalar karancin abinci