A cikin shirin za a ji cewar wasu mata 'yan kunar bakin wake sun hallaka mutane da dama a wasu hare-hare uku da suka kai wata kasuwa a Chadi. Za kuma a ji karin haske kan zaben gwamna a jihar Bayelsa da ke kudancin Najeriya inda rahotanni ke cewar an samu asarar rai.