A cikin shirin za a ji cewa a yayin da Najeriya ke ci gaba da fuskantar barazana a bangaren tsaro, majalisar tsoffin shugabannin kasar sun gana da Shugaba Muhammadu Buhari a makon da ke shirin karewa. Kungiyar dalibai a Jamhuriyar Nijar ta shiga takun saka da gwamnatin kasar bayan da ta ayyana matakin rijistar daliban da ke son jarabawar shiga jami'a ta intanet.