A cikin shirin za a ji cewa shugabannin yankin Kudu maso gabashin Najeriya sun zargi gwamnatin tarayya da yin rikon sakainar kashi ga matsalar tsaron da ke addabar Najeriya. A Jamhuriyar Nijar kuwa fursunonin a gidan yarin Damagaram ne suka koka da karancin abincin bude baki a wannan watan na Ramadan.