A cikin shirin za a ji cewa a Najeriya magoya bayan jam'iyyar APC mai mulkin kasar ne ke ci gaba da mayar da martani tun bayan kammala babban taronta a karshen mako. Sai dai jihar Kano mafi yawan al'umma a arewacin Najeriya ba ta samu wasu gwaggwaban mukamai na jagorancin jam'iyyar ba.