A cikin shirin za a ji cewa cibiyoyin ketare da ke tallafa wa Ghana da kudi don gudanar da allurar rigakafin yara kanana sun sanar da dakatar da gudunmawarsu kan nan da shekarar 2026, kana makiyaya a jihar Gaya na Jamhuriyar Nijar sun shiga halin damuwa bayan gwamnatin Jamhuriyar Bénin ta dauki matakin rufe iyakokin kasarta ga makiyayan kasar Nijar.