A cikin shirin za a ji cewa a Najeriya ana mayar da martani kan matakin gwamnatin kasar da ta ce daga farkon watan Disamba duk ma’aikacin da bai yi alurarar corona ba, ba za a bar shi ya shiga ofis ba, a yayin da a Jamhuriyar Nijar kungiyar Alternative Espace Citoyen tare da taimakon masu hannu da shuni ta buda wata makarantar horas da yara matasa maza da mata kan siyasa da dimukuradiyya.