A cikin shirin za a ji cewa a Jamhuriyar Nijar Bangarori dabam-daban ne ke cigaba da korafin rashin ganin wani kokarin gwamnatin kasar a zahiri don yaki da matsalar ambaliyar da ke haddasa salwantar rayukan jama'a, a yayin da a Najeriya takkadama ta barke kan alakar rukiya yar zamani da kuma harkokin bori.