A cikin shirin bayan an saurari labaran duniya za a ji cewa a Najeriya ci gaba da martani kan daga muhawarar kudurin dokar man fetur da majalisar dokokin kasar ta yi zuwa shekarar badi. A Jamhuriyar Nijar kuwa shugabannin kungiyoyin farar hulla ne suka koka da yadda hukumomi ke nuna musu wariya wajen tauye su gudanar da tarukan gangami da zangar lumana.