A cikin shirin za ji cewa kwanaki hudu bayan wani kazamin harin 'yan bindiga kan jirgin kasan nan mai jigilar fasinja daga Kaduna zuwa Abuja a Najeriya, gwamnan Kaduna Malam Nasiru el-Rufa'i ya yi tozali da shugaban kasa a yau don tattauna matsalolin tsaro da ke kara ta'azzara a jihar.