A cikin shirin za a ji cewa al'umma a jihar Zamfara mazauna Kaduna na mayar da martani bayan wani kazamin harin 'yan bindiga kan hanyar Kaduna zuwa Abuja da ya halaka wani tsohon dan takarar gwamna. A jamhuriyar Nijar kuwa sama da yara dubu 50 ne ba sa zuwa makaranta a sassa dabam-daban na jihar Tillaberi da ke yammacin kasar sakamakon matsalolin tsaro da ke addabar yankin.