A cikin shirin za a ji kotu a Birtaniya ta dakatar da aiwatar da hukunci da aka yanke inda Najeriya za ta biya sama da dala biliyan 9 ga kamfanin nan na P&ID da ke tonon iskar gas sakamakon wata takaddama tsakanin kamfain da Najeriya. A Jamhuriyar Nijar kuwa ma'aikatar cikin gida ce ta ce ta soke tarukan Kongre da jam'iyar adawar adawa ta Moden Lumana Afirka suka yi saboda keta doka.