1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Lambar yabo a ranar 'yancin 'yan jarida

Binta Aliyu Zurmi
May 3, 2021

'Yar jarida daga Najeriya ta samu lambar yabo ta tashar DW albarkacin ranar 'yancin 'yan jarida ta duniya.

https://p.dw.com/p/3st13
Freedom of Speech Award 2021 | Preisträgerin Tobore Ovuorie aus Nigeria
Hoto: Elvis Okhifo/DW

Wata 'yar jarida mai binciken kwakwaf da ke tarayyar Najeriya, Tobore Ovuorie, ta ci lambar yabo ta DW kan fadin 'yancin albarkacin baki na wannan shekarar ta 2021.

Tobore Ovuorie, tana cikin 'yan jaridu masu binciken kwakwaf da ma bin diddgi a Najeriya. Burinta shi ne tsage gaskiya da kuma bankado boyayyun al'amura. 

A shekarar 2013, Ovuorie ta yi kasadar shiga aikin karuwanci na tsawon watanni bakwai da nufin bankado yadda ake safarar mata domin aikin karuwanci da kuma sayar da sassan jiki bil Adama.

Wannan kasada ta sai da rai da Ovuorie ke yi, shi ne ya janyo hankalin shugaban tashar Deutsche Welle, Peter Limbourg, har ya ba ta kyautar ta wannan shekara.