1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya ta samu koma baya a sha'anin mulki

October 24, 2024

Cibiyar Mo Ibrahim mai bin diddigin shugabanci na gari a nahiyar Africa ta ce Najeriya ta samu gaggarumin koma baya a shugabancin al'umma a shekaru 10 da suka gabata.

https://p.dw.com/p/4mCaJ
Elfenbeinküste 2019 Ibrahim Governance Weekend in Abidjan
Hoto: DW/F. Quenum

Wani sabon rahoton shugabanci a nahiyar Africa ya ce tarayyar Najeriyar ta zama baya ga dangi kan sha'anin mulki a tsakanin al'umma.

Rahoton Mo Ibrahim da ya yi nazarin mulkin a tsakanin kasashen Afirka 54 ya ce, Najeriyar ta gaza a fannoni daban daban cikin harkar mulkin.

Kasar dai ta koma ta 11 cikin mafi lalacewa a nahiyar sakamakon rashin tsaro da tattalin arziki a shekaru 10 da suka gabata.

Gidauniyar Mo Ibrahim a taron manema labarai
Hoto: Mo Ibrahim Foundation

Rahoton ya kuma ce Najeriyar ta gaza yakar cin hanci da rashawa, sannan kuma ta gaza tabbatar da yancin a wataya ta fannonni daban daban.

Rahoton dai na kara fitowa fili da yadda tsarin demokaradiyya ke neman gaza kai wa ga biyan bukatun miliyoyi cikin kasar dake da babban fata kansa.

Isa Yuguda tsohon gwamnan jihar Bauchi da kuma ya ce abun da ke akwai a tarayyar Najeriya na da ruwa da tsaki da gazawa ta tsohuwar gwamnatin kasar.

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya
Hoto: Nigeria Prasidential Villa

Kokari na komawa tushe ko kuma neman rushe lamura dai, kusan daukacin shekarun 10 da suka gabata sun faru ne a karkashin masu tsintsiyar tarayyar Najeriyar.

Akwai dai zargin APC da ta karbi mulki a shekara ta 2015 a cikin alkawarin gyara kurakuran PDP ta kare da kara rusa daukacin ginshikin harkokin mulkin.

To sai dai kuma abun da ke faruwa a shekarun APC a tunanin Abdullahi Umar Ganduje shugaban jam'iyyar APC mai mulkin kasar, na kama da kokarin daukar saiti cikin kasar da ke tangal tangal.

Mo Ibrahim
Hoto: Alex Wong/Getty Images

Fatan sauyi zuwa gaba, koma nisa a cikin rudani dai, tarayyar Najeriyar ta dade tana karatun sauyin amma kuma tana kara ganin sauyi irin na mai haka rijiya.

Farfesa Attahiru Jega kwarrare ne a harkar mulki da siyasa, kuma ya ce mayar da siyasar zuwa sana'a ne ya kai kasar cikin rudun da ke da girman gaskiye.

Najeriyar dai ta bi sahu cikin lalacewar da kasashe irin su Niger, da Burkina Faso da Mali da ke karkashin mulkin soja suka yi.