1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mali: Jamus ta sanar da karshen ayyukan sojojinta a Mali

December 12, 2023

Kasar Jamus ta sanar da ficewa daga shirin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya da aka fi sani da MINUSMA, a kasar Mali, kamar yadda hukumomin Bamako su ka bukaci hakan.

https://p.dw.com/p/4a5YA
Hoto: Nana Ehlers/Bundeswehr/dpa/picture alliance

Kasar Jamus ta sanar da  ficewar sojojinta  daga shirin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya da aka fi sani da MINUSMA, a kasar Mali, kamar yadda  shugabannin mulkin sojin Bamako suka bukaci hakan daga hukumomin Berlin.

Tuni dai tawagar karshe ta dakarun Jamus akalla 142 suka bar sansaninsu da ke birnin Gao dake arewa maso gabashin kasar ta Mali, a wata sanar wa da ma'aikatar tsaron Jamus ta fitar.

Sanarwar ta kara da cewa ragowar sojojin Jamus 4 da suka rage a birnin Bamako za su fice daga kasar, zuwa ranar lahadi 17 ga watan disambar 2023.