1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus da Faransa sun gargaɗi 'yan ƙasashensu a Mali

April 2, 2012

Ana cikin halin rashin sanin tabbas a Mali a daidai lokacin da shugabannin ƙasashen yamnmacin Afirka suka bude taro akan Mali a birnin Dakar.

https://p.dw.com/p/14WUD
Supporters of Mali's junta participate in a demonstration against regional bloc ECOWAS (Economic Community of West African States) at the international airport of Bamako March 29, 2012. Jets carrying West African presidents for a meeting with Mali's new military leaders were forced to turn back mid-flight on Thursday after hundreds of supporters of last week's coup invaded Bamako's main runway. An official from regional bloc ECOWAS said the meeting, aimed at pressuring coup leaders to swiftly restore constitutional rule after they ousted President Amadou Toumani Toure, could be rescheduled for Friday if security allowed. REUTERS/Luc Gnago (MALI - Tags: POLITICS CIVIL UNREST MILITARY) // Eingestellt von wa
Hoto: Reuters

Ministan harkokin wajen Faransa Alain Juppe ya ce halin da ake ciki a Mali yana ƙara taɓarɓarewa sai dai ya ce Faransa ba za ta tura dakarunta zuwa ƙasar da ta taɓa yi wa mulki mallaka ba. Juppe wanda ke birnin Dakar yanzu don halartar bikin rantsar da sabon shugaban Senegal Macky Sall, da aka yi a wannan Litinin, ya faɗa wa manema labarai cewa ana cikin wani hali mai hatsri a Mali saboda haka ya gargaɗi dukkan Faransawa da kasancewar a Mali ba ta da wani muhimmanci da su fice daga ƙasar. Ya ce Faransa za ta iya taimakawa da kayan aiki ko ba da horo ga sojojin Mali amma ba ta girke dakarunta ba, musamman kasancewa ana garkuwa da wasu Faransawa shida a yankin, rayuwarsu ka iya faɗawa cikin wani hatsari. Shi ma ministan harkokin wajen Jamus Guido Westerwelle a cikin wata sanarwa ya yi kira ga sojoji a Mali da su gaggauta maido da mulkin doka tare da kawo ƙarshen faɗan da ake yi a arewacin ƙasar ta Mali. Wani kakakin ma'aikatar wajen Jamus ya ce gwamnatin ƙasar na kira ga dukkan Jamusawa da su guji zuwa Mali kana waɗanda ke cikin ƙasar kuma su yi ƙoƙarin ficewa. Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugabannin Yammacin Afirka su fara wani taro a birnin Dakar na ƙasar Senegal, inda suke tattaunawa akan halin da ake ciki a Mali.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Halima Balaraba Abbas