1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zanga kan matsalar satar mai a Najeriya

Uwais Abubakar Idris RGB
September 8, 2022

Kungiyar ma’aikatan man fetir da iskar gas sun gudanar da zanga-zangar lumana a Abuja domin nuna damuwarsu kan matsalar satar danyen mai da ake yi a Najeriya.

https://p.dw.com/p/4GbKG
Symbolbild | Nigeria Gaspipeline
Hoto: Florian Plaucheur/AFP/Getty Images

Kungiyar manyan ma’aikatan man wato PENGASSAN sun gudanar da zanga-zangar lumana a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya, yunkuri ne na nuna damuwarsu a kan karuwar satar danyen mai da ake yi a kasar da suka ce, yana neman durkusar da tattalin arzikin Najeriyar da ta dogara a kan arzikin man. 

Ci gaba da ta’azzarar da satar man fetir da ake yi a Najeriya da a yanzu ya wuce hankali da tunanin mahukuntan Najeriyar, wannan ya kai ga tunzura 'ya'yan kungiyar ta manyan ma’aikata da suka kai ga fitowa, don ganin an dauki mataki na hakika a kan lamarin. Ta dai kai ga gwamnatin Najeriyar bayyana cewa kashi casa'in da biyar, na man da ake hakowa a tashar hako mai ta Bonny, sace shi ake yi.

BdTD l Nigeria,  Ölteppich bei Santa Barbara in Nembe
Ta'asar masu fasa bututun mai a jihar BayelsaHoto: Temilade Adelaja/REUTERS

Amma baya ga wannan mummunan dabi’a da ake yi a wasu jihohin da ake hako man Najeriyar, a baiyane take cewa, matsalar ta kai wa kowa a wuya domin duk da amincewar Najeriya da kungiyar kasashe masu arzikin man fetir ta OPEC, na ta hako ganga miliyan 1.8 amma ganga milyan 1,200 take iya samarwa.

Nigeria Umwelt l Undichte Ölleitungen verseucht das Land im Nigerdelta
Yankin Naija Delta na fama da matsalar malalar maiHoto: Friedrich Stark/imago

Bayanai sun nuna cewa, Najeriyar ta yi asarar dala biliyan goma a watani shida na wannan shekara a fannin satar mai. Akwai sauran kungiyoyi na kwadago da suka shiga zanga-zangar, domin nuna goyon bayansu. Kungiyar mai suna PENGASSAN na zargin cewa akwai hannu na mutanen da dama, musamman al'umman da ke a wuraren da ake hako man fetir, abin da ya kama hanyar durkusar da tattalin arzikin Najeriyar.

Daga batun dama zanga-zangar zuwa ga hedikwatar ‘yan sandan Najeriya da kamfanin albarkatun man a kasar, na nuna cewa, ya fa isa haka a wannan aiki na masu halin bera da ke sace man Najeriya suna durkusar da tattalin arzikin kasar. Yanzu kallo ya koma sama inda ake jiran yadda za ta kaya a kokarin magance wannan matsalar.