1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

HRW na zargin sojan Burkina Faso da kisan fararen hula

January 25, 2024

Kungiyar kare hakkin dan'Adam ta Human Rights Watch ta zargi sojojin Burkina Faso da kisan fararen hula da dama a yakin da suke da kungiyoyin 'yan ta'adda.

https://p.dw.com/p/4beGl
HRW na zargin sojojin Burkina Faso da kisan fararen hula
HRW na zargin sojojin Burkina Faso da kisan fararen hulaHoto: Dracorius White/ZUMAPRESS/picture alliance

A wani rahoton da ta fitar a ranar Alhamis 25.01.2024, Human Rights Watch ta ce tana zargin sojojin Burkina Faso da kisan akalla fararen hula 60 a hare-haren da suke ikirarin sun kai wa mayakan jihadi a wasu sassan kasar.

Karin bayani: An kashe fararen fula a Burkina

Kungiyar ta ce ta yi hira da shaidu da dama kan wannan lamari da ya auku a cikin watan Ogustan shakarar 2023, kana kuma tana ci gaba da gudanar da bincike a kan hotuna da bidiyo da kuma hutunan tauron dan'Adam da ta tattara domin hakikance gaskiya.

A cikin rahoton kungiyar ta ambato mazaunin wani kauye da ake kira Bouro inda ake kyatata zaton an kashe mutane 28 a sakamakon hare-haren, yana cewa gwamnatin kasar na daukar yankinsu a matsayin na 'yan ta'adda, sannan kuma suna tsoron zuwa asibiti idan suka samu raunika sakamakon hare-haren da sojoji ke kai wa ta sama.

Karin bayani: Burkina Faso: Kara wa'adin dokar ta-baci

A baya-bayan dai Burkina Faso na amfani da sabbin dabarun yaki da 'yan ta'adda, inda take farautarsu da jirage marasa matuka sannan kuma a watsa faya-fayan bidiyon a gidan talabijin na kasar don nuna kuzazin da sojoji ke yi.