1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Ta'addanci

Shawo kan matsalar tsaro a Burkina Faso

Lateefa Mustapha Ja'afar
May 13, 2023

Matsalar masu ikirarin jihadi da makamai, ya sanya Burkina Faso kara wa'adin dokar ta-bacin da ta sanya a yankuna takwas cikin 13 da kasar ke da su a da watanni shida.

https://p.dw.com/p/4RJOJ
Burkina Faso | Tsaro
Matsalar rashin tsaro, ta raba mutane da dama da muhallansu a Burkina FasoHoto: AP/picture alliance

Majalisar dokokin rikon kwaryar ta Burkina Fason ce ta amince da wannan kudiri ba tare da hamayya ba, inda a yanzu dokar ta-bacin za ta kawo karshe a ranar 29 ga watan Oktabar bana.  Ministar shari'a na kasar Bibata Nebie Ouedraogo ta bayyana cewa, dokar ta-bacin za ta taimaka gaya wajen shawo kan matsalar tsaro da kuma bai wa jami'an tsaro damar yin aiki tukuru. Dokar da gwamnati ta sanya a watan Maris na wannan shekara, an yi ta ne domin taimakon jami'an tsaro musamman a binciken gida-gida da suke yi dare da rana domin gano bata-gari da kuma takaita zirga-zirga da taruwar jama'a.