A wannan makon mun tattauna ne kan ayyukan da suka kamata mata da matasa su himmatu da su domin samun dumbin ladar da watan Azumi ke kunshe da su. Mun tattauna da Sheikh Halliru Maraya, Malamin addinin Islama a Kaduna da kuma Malama Juwairiyya Usman Suleiman, ita Malama da ke ilimantar da jama'a a jihar Bauchi a Najeriya.