Salon rayuwa
Gaskiyar Magana: Ceto darajar naira a Najeriya
Talla
A shirin na wannan makon mun tabka muhawara a kan yadda za a ceto darajar naira daga durkushewar da ta ke yi, lamarin da ke jefa al'ummar Najeriya a cikin wani mawuyacin hali. Mun tattauna da Farfesa Ahmed Adamu, masanin tattalin arzikin kasa a Najeriya da kuma Muhammad Almustapha Naira, mataimakin mai kula da dokokin kungiyar 'yan chanji ta Abuja, babban birnin Najeriya.