1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ebola na ci gaba da lakume rayuka

August 15, 2014

Cutar Ebola mai saurin kisa da ta addabi yankin yammacin Afirka ta lashe rayukan al'ummar wannan yanki sama da 1,100 yayin da wasu sama da 2,100 suke dauke da kwayar cutar.

https://p.dw.com/p/1CvZ3
Hoto: picture-alliance/dpa

Hukumar Lafiya ta Duniya wato WHO ta sanar da cewa adadin wadanda cutar Ebola ta lakume rayukansu a yammacin Afirka na karuwa. Kiyasin da hukumar ta WHO ta fitar na nuni da cewa kawo yanzu mutane sama da 1100 ne cutar ta Ebola ta hallaka a yankin yammacin Afirka sakamakon rahoton karin mutuwar wasu mutane 74 da aka samu tsakanin 12 da 13 ga wanna wata na Agusta da muke ciki a kasashe hudun da ke fama da cutar. Kiyasin na hukumar ta WHO ya kuma nunar da cewa an samu sababbin rahotannin bullar cutar har sama da 150 a kasashen Gini da Laberiya da Saliyo da kuma Najeriya wanda ya kawo adadin wadanda ke dauke da cutar a yanzu haka zuwa 2,127 a tssakanin kasashen hudu. Yanzu haka dai akwai fargaba mai tsanani ta barkewar yunwa a Laberiya sakamakon wannan bala'i na annobar cutar Ebola.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Umaru Aliyu