1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dokar ta-baci kan fyade a Najeriya

June 12, 2020

Gwamnoni a Najeriya, sun kaddamar dokar ta-baci a kan matsalar fyade ga mata da ke ci gaba da karuwar a kasar a wannan lokaci da yankuna da dama ke dokar kulle.

https://p.dw.com/p/3dho4
Südafrika Johannesburg Demonstration Vergewaltigung
Hoto: picture-alliance/dpa

A kusan karshen yinin ranar Alhamis ne dai gwamnonin Najeriya 36 suka fitar da matsaya a kan wadanda ke aikata wannan kazamar dabi'a, bayan zanga-zangar da ta karade kasar da ke nuna gajiya da lamarin.

A jawabin da ya yi wa 'yan kasar albarkacin cikar kasar shekaru 21 da kama tafarkin dimukuradiyya, Shugaba Muhammadu Buhari ya ce ya kadu matuka da yadda fyade ke karuwa a Najeriyar, musamman na kananan yara mata.

Shi ma ministan shari'ar kasar, Abubakar Malami, ya ce nan ba da jimawa ba za a kaddamar da kwamiti a dukkanin manyan ma'aikatu na gwamnatin tarayya wadanda za su tsara hanyoyin sauya hukunci kan cin zarfin na mata, hukuncin kuma da zai dace da ko'ina a duniya.