1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Amurka za ta kara karfin soja a Gabas ta Tsakiya

August 3, 2024

Amurka ta ce za ta aike da wata rundunar musamman ta masu amfani da jiragen yaki zuwa yankin Gabas ta Tsakiya, wani abu da ta ce na fadada ayyukan sojinta ne a yankin.

https://p.dw.com/p/4j4UI
Sakataren tsaron Amurka, Lloyd Austin
Sakataren tsaron Amurka, Lloyd AustinHoto: Alex Wong/Getty Images

Ma'aikatar tsaro ta Pentagon, ta ce Amurkar za ta yi hakan ne domin hana rincabewar al'amura sakamakon barazanar da kasar Iran da masu alaka da ita ke yi na yiwuwar kai hare-hare.

Tun bayan kazamin harin ranar bakwai ga watan Oktoba da kungiyar Hamas ta kaddamar a kan Isra'ila da ya yi sanadin yakin da ake ciki a Gaza ne dai Sakataren Tsaron Amurkar Loyd Austin ya jadda shirin Amurka na kare mutane da muradunta a yankin.

Rikici dai na kara kazanta a yankin Gabas ta Tsakiya, bayan kisan jagoran kungiyar Hamas Ismail Haniyeh a Iran da ma wani babban kwamandan Hezbollah a Beirut babban birnin kasar Labanan.