1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Yiwuwar hana shiga Amirka

Lateefa Mustapha Ja'afar
January 22, 2020

Shugaban Amirka Donald Trump ya bayyana cewa gwamnatinsa na shirin kara yawan adadin kasashen da za ta hana al'ummominsu shiga cikin kasar.

https://p.dw.com/p/3WfBb
Weltwirtschaftsforum 2020 in Davos | Donald Trump, Präsident USA
Hoto: picture-alliance/AP Photo/E. Vucci

Shugaba Donald Trump ya bayyana aniyar tasa ne yayin da yake jawabi a zauren babban taron tattalin arziki na duniya a birnin Davos na kasar Switzerland. Mujallar Wall Street Journal ta Amirkan ta ruwaito cewa, hanin zai shafi kasashe bakwai da suka hadar da Najeriya da ke zaman kasa mafi yawan al'umma a nahiyar Afirka da kuma wasu kasashen na AFirka da Asiya, kana su ma kasashen Belarus da Iritiriya da Kirgistan da Bama da Sudan da kuma Tanzaniya.