1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Abu Namu: Shekaru biyar da sata 'yan matan Chibok

Ramatu Garba Baba MNA
April 29, 2019

Shirin na wannan makon ya mayar da hankali kan batun cika shekaru biyar da sace ‘yan matan sakandare na garin Chibok a jihar Borno.

https://p.dw.com/p/3HcSX
Nigerias Terror geht weiter
Hoto: DW/K. Gänsler

Sata 'yan matan Chibok ta yi matukar jan hankalin al'ummar duniya. Shekara biyar da faruwar lamarin ma dai ana ci gaba da tafka mahawara kan wannan batu da ya shiga cikin jerin munanan abubuwa da suka taba faruwa a tarihi.
Shirin Abu Namu zai mayar da hankali kan batun cika shekaru biyar da sace ‘yan matan sakandaren na garin Chibok a jihar Bornona Najeriya. Kamar yadda watakila aka sani an sace ‘yan matan 276 ne daga makarantarsu ta kwana a ranar 14 ga watan Afrilun 2014.