1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Share fagen ganawar Trump da Kim

Lateefa Mustapha Ja'afar
May 30, 2018

Wanin babban na hannun daman shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya isa birnin New York na Amirka.

https://p.dw.com/p/2yfoL
Südkorea Abreise Kim Yong Chol
Kim Yong Chol mataimakin shugaban jam'iyyar Workers Party mai mulki a Koriya ta ArewaHoto: picture-alliance/AP Photo/Korea Pool/Newsis

Ziyarar ta Kim Yong Chol wanda ke zama wani ja gaba a gwamnatin Koriya ta Arewan, na zaman ta share fagen tattaunawar da za a yi tsakanin shugaban Amirkan Donald Trump da kuma takwaransa na Koriyar ta Arewan Kim Jong Un. Kim Yong Chol dai zai gana da sakataren harkokin wajen Amirka Mike Pompeo a wata ziyara da ke zaman ta farko da wani babban jami'in Koriya ta Arewa ya kai Amirka tun tsahon shekaru 18 din da suka gabata. A ranar 12 ga watan Yuni mai zuwa ne dai ake sa ran shugannin biyu za su yi wannan ganawa mai matukar tarihi a tsakaninsu.