1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaɓen yan majalisun dokoki a Burkina Faso

May 6, 2007
https://p.dw.com/p/BuM1

Yau ne jama´a ƙasar Burkina Faso, ke zaɓen yan majalisun dokoki.

Baki ɗaya, kussan mutane milion4 da rabi, ya cencenta su kaɗa ƙuri´a domin zaɓen yan majalisu 111 daga jerin yan takara kussan dubu 4, da su ka hitto daga jam´iyun siyasa 47 na ƙasar.

Saidai akwai alamun jama´a na nuna halayen ko in kulla da wannan zaɓe , ta la´akari da yadda,har jajibirin zaɓe, mutane ƙalilan su ka karɓi katocin zaɓe ,inji shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta Musa Michel.

A tsawan kwanaki 21, na yaƙin neman zaɓe jama´iyun adawa, da su ka kasa haɗa kai, domin fuskantar jama´iyar shugaba Blaise Campaore, sun bayyana matsalolin da gawmanti mai ci yanzu, ta tsunduma jama´ar ƙasa a cikinsu.

Fatara da talauci, rashin kyaukayawan matakan tsaro, da al´ammuran cin hanci da karɓar rashawa injin yan adawar, sun zama ruwan dare a Burkina Faso.

A na kyauttata zaton bada sakamakon wannan zaɓe, ranar juma´a mai zuwa.