1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zartar da hukuncin kisa a Iran

Usman Shehu Usman
October 28, 2024

Hukumomi kasar Iran sun aiwatar da hukuncin kisa kan wani dan kasar mai ruwa biyu Jamshid Sharmahd mutumin dake Bajamushe mai asalin kasar ta Iran bayan samun sa da laifin cin hanci da rashawa

https://p.dw.com/p/4mKE9
Iran | Deutsch-Iraner Djamshid Sharmahd in einem Teheraner Revolutionsgericht
Hoto: Koosha Falahi/Mizan/dpa/picture alliance

Wata sanarwa da hukumomin shari’a a Iran suka fitar, ta ce bayan yin nazari bisa shari’ar da aka yi, a safiyar wannan Litinin mahukuntan sun bada izinin zartar da hukuncin kamar yadda kotu ta yanke. Dama tun a shekara ta 2020 da aka sameshi da laifi kuma tun wannan lokacin Jamshid Sharmahd yake zama a gidan yari kafin hukumomi su zartar da hukucin a wannan Litinin. Kasar Iran na cikin kasashen duniya da har yanzu ke zartar da hukuncin kisa. Masu kare hakkin jama'a da 'yan fafitika, sun jima suna gangami a Iran da kuma musamman a kasar Jamus don neman a sako Jamshid Sharmahd daga gidan yari, abin da bai samu ba har izuwa wannan Litinin da aka zartar masa da hukuncin kisa kamar yadda a baya kotu ta bada umarni.