1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zargin 'yan jarida da cin amanar Yuganda

Yusuf Bala Nayaya
November 23, 2017

Mutane takwas an kamasu a ranar Talata lokacin da 'yan sanda suka kai wani simame gidan jaridar ta Red Pepper da ke watsa labaranta a harshen Ingilishi da harshen al'ummar kasar.

https://p.dw.com/p/2oABh
Uganda Medienfreiheit Proteste 20.05.2013
Hoto: Reuters

Editoci da daraktoci takwas na gidan wata fitacciyar jarida a kasar Yuganda an tuhumesu da laifi na cin amanar kasa bayan da jaridarsu ta fitar da wani labari da ya zargi hannun Shugaba Yoweri Museveni a kokarin shirya kifar da takwaransa na kasar Ruwanda Paul Kagame, kamar yadda lauya da ke kare shugaban ya bayyana a wannan rana ta Alhamis.

Mutanen takwas an kamasu a ranar Talata lokacin da 'yan sanda suka kai wani simame gidan jaridar ta Red Pepper da ke watsa labaransa a harshen Ingilishi da ma harshen da al'ummar kasar ke amfani da shi. A ranar Laraba kuma aka tuhumesu da laifi na cin amanar kasa, laifin da ka iya kaisu ga gidan kaso tsawon shekaru bakwai. Ko da yake sun musanta.