1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-Zangar ƙasar Masar

February 14, 2011

Masu zanga-zangar neman kawo sauyi a Masar sun koma dandalin Tahrir bayan da sojoji suka fatattake su

https://p.dw.com/p/10Gyr
Masu zanga-zanga a dandalin Tahrir na MasarHoto: dapd

Masu jerin gwanon nuna adawa da gwamnatin daya tilastawa shugaba Hosni Mubarak na Masar yin murabus sun sake komawa dandalin Tahrir da ke tsakiyar birnin al-Qahira, bayan tunda farko sojoji sun umarce su da ficewa daga wurin. Sojojin da suka karɓi ragamar jagoranci a ƙasar ta Masar bayan murabus na Mubarak a ranar Jumma'ar da ta gabata, sun tilastawa rukunin ƙarshe na masu zanga zanga su fice daga dandalin Tahrir, a yayin da rundunar sojin ke ƙoƙarin tabbatar da ikon ta da kuma mayar da bin doka da oda a ƙasar. Kimanin Misirawa 40 ne jami'an 'yan sandan ƙasar suka yiwa ƙawanya a dandalin daya taka rawar da ta kai ga hamɓarar da mulkin shugaba Hosni Mubarak a ranar Jumma'a.

Bayan murabus ɗin ne kuma sojojin suka yi gargaɗi game da duk wani taron jama'a, kana suka haramta duk wani nau'i na yajin aiki. A cikin wata sanarwar da rundunar sojin ta fitar a jiya Lahadi, ta ambata Muhammad Husseini Tantawi a matsayin wanda zai shugabanci majalisar sojin da za ta kula da lamuran ƙasar - har na tsawon watanni shidda ko kuma har bayan gudanar da zaɓukan majalisar dokoki da kuma na shugaban ƙasa.

A halin da ake ciki kuma, firaministan ƙasar ta Masar Ahmad Schafik ya tabbatar da cewar, shugaba Mubarak na ci gaba da gudanar da harkokin sa ne a wurin shaƙatawar nan na Sharm el-Sheikh:

" Shugaba Mubarak dai a yanzun nan da nake magana da kai yana Sharm el-Sheikh. Har dai ya zuwa wannan safiyar, abinda na sani kenan, kuma na yi amannar har yanzu yana can."

Mawallafi : Saleh Umar Saleh

Edita : Mohammad Nasir Awal