1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Zanga-zanga ta sake barkewa a kasar Sudan

Abdoulaye Mamane Amadou
October 30, 2021

Masu rajin kare mulkin farar hula a Sudan sun soma wata gagarumar zanga-zanga a wannan Asabar, a ci gaba da nuna kyama da matakin kwace mulki da karfin tuwo da sojoji suka yi a farkon wannan mako.

https://p.dw.com/p/42NWx
Nach Militärputsch im Sudan
Hoto: Marwan Ali/AP/picture alliance

Shaidun gani da ido sun ce jama'a da dama ne suka fito kan tituna a  Omdourman da Khartum, domin amsa kiran masu fafutikar ganin an sake mayar da mulki a hannun farar hula a Sudan. A ranar Litinin da tagabata ne jagoroan juyin mulkin Janar Abdel Fattah al-Burhane ya bayyana rushe daukacin hukumomin gwamnatin rikon kwarya da ke karkashin jagorancin fararen hula baya ga kama firaministan wucin gadi, lamarin da ya kara jefa kasar cikin rudanin siyasa.

Ko da yake an sallami hamabararren firaministan Abdallah Hamdok, amma ana ci gaba da tsare wasu da dama daga cikin mambobin gwamnatinsa, lamarin da kuma ya kara janyo wa gwamnatin mulkin soja mummnan suka daga kasashen duniya.