1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burkina Faso: 'Yan ta'adda sun kashe mutum 79

Abdourahamane Hassane
June 14, 2022

Shugaban gwamnatin rikon kwarya na Burkina Faso, Laftanar Kanar Paul Henri Sandaogo ya ayyana zaman makoki na kwanaki uku a fadin kasar. Bayan harin ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 79.

https://p.dw.com/p/4CguN
Burkina Faso Ougadougou | Amtseinführung - Paul-Henri Damiba
Hoto: Burkina Faso Presidency Press Service/REUTERS

A daren Asabar zuwa Lahadi wasu mutane dauke da makamai suka kashe  fararen hulan a wani hari da suka kai a kauyen Seytenga dake a rewacin Burkina Fason kan iyaka da Nijar. Koi'na a cikin ofisoshi gwamatin na cikin gida da ketare an yi kasa-kasa da tuttocin kasar domin girmama wadanda suka mutu.Wanda ke daya daga cikin hare-hare mafi muni da aka kai, tun bayan da sojoji suka karbi mulki a cikin watan Janairun da ya gabata.