1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

A Afirka ta Kudu wasu jama'ar sun soma kada kuri'a

Abdourahamane Hassane
May 28, 2024

A Afirka ta Kudu wasu jama'ar da ba za su iya halartar rufunan zabe ba tuni da suka fara kada kuria, a zaben 'yan majalisar dokoki

https://p.dw.com/p/4gMNQ
Hoto: Michele Spatari/AFP/Getty Images

 Masu kada kuri'a miliyan 27 ne aka yi rajista. Fiye da miliyan daya da rabi suka yi rajista don kada kuri'a da wuri a kwanaki biyu kafin zaben.Tun bayan zaben Nelson Mandela, jam'iyyar ta lashe dukkanin zabukan kasar da gagarumin rinjaye,To amma a wannan karon jam'iyyar ANC na fuskantar barazanar rasa rinjaye a majalisar dokokin kasar, inda take tsakanin kashi 40% zuwa 47%. a hasashen da wasu kafofi masu zaman  kansu suka yi.