1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yaɗuwar rikicin Siriya zuwa Lebanon

May 26, 2013

Mutane da dama sun sami rauni bayan harba wata roka da aka yi a anguwar ''yan Shi'a da aka yi birnin Beirut na Lebanon.

https://p.dw.com/p/18eGo
Supporters of Hezbollah and relatives of Hezbollah member Hussein Ahmad Abu Hasan carry his coffin during his funeral in Beirut's suburbs May 21, 2013. On a country road in Lebanon's northeast, traffic is heavy; ambulances screech by, sirens blaring, and cars packed with mourners follow coffins as Hezbollah brings wounded fighters home from Syria, and its dead. Having long denied its engagement in Syria behind President Bashar al-Assad, Hezbollah has committed itself this week to the fight for the strategic small town of Qusair, sending hundreds of men and losing dozens wounded and between 20 and 50 killed. Picture taken May 21, 2013. To match Analysis SYRIA-CRISIS/HEZBOLLAH REUTERS/Issam Kobeisy (SYRIA - Tags: POLITICS CIVIL UNREST)
Hoto: Reuters

Wasu makamai masu linzami guda biyu da aka harba a wannan Lahadin (26.05.13), a wata unguwar da galibin mazaunanta nabiya darikar Shi'a ne da ke birnin Beirut na kasar Lebanon, ya janyo rauni ga mutane da dama, kamar yadda mazauna unguwar suka bayyana. Wannan harin dai ya zo ne yini daya kachal bayan da jagorar kungiyar Hizbullah ta mabiya darikar Shi'ah a kasar ta Lebanon, Hassan Nasrullah ya bayyana cewar, mayakansa za su ci gaba da yaki a kasar Siriya har sai gwamnatin kasar a karkashin jagorancin shugaba Bashar al-Assad ta sami nasara.

Harin kuma shi ne irinsa na farko da aka kaiwa yankin da galibinsa mabiya darikar Shi'ah ne a birnin na Beirut, tun bayan barkewar yakin basasa a kasar Siriya, wadda ke makwabtaka da Lebanon, wanda kuma ya kara zafafa yakin bangaranci a cikin gidan Lebanon din. 

Duk da cewar babu wani mutum ko wata kungiyar da ta dauki alhakin kaddamar da harin,  Brigadier Selim Idris, na kawancen 'yan adawar Siriya da ke samun goyon bayan kasashen yammacin duniya ya shaidawa tashar telebijin ta al-Arabiyya cewar babu hannun dakarunsa wajen kai harin, kana ya bukaci 'yan tawayen da su ci gaba da yaki a cikin Siriya kawai ba tare da tsallakawa domin kai hari a wata kasar ketare ba.

 A halin da ake ciki kuma ministan harkokin wajen Faransa  Laurent Fabius, ya yi Allah wadai da rikicin da ya barke a Lebanon yana mai cewar bai kamata a kyale rikicin Siriya ya bazu zuwa kasar ba.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita        : Usman Shehu Usman