1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yau Litinin an kaddamar da sabuwar majalisar dokokin Somaliya

August 20, 2012

A karon farko cikin shekaru 20, ana kaddamar da majalisr dokokin Somaliya a birnin Mogadishu.

https://p.dw.com/p/15t5e
Somalia's President Sheikh Sharif Ahmed (L) and Prime Minister Abdiweli Mohamed Ali attend the Somalia Conference at Lancaster House in London February 23, 2012. Clinton on Thursday threatened sanctions against anyone blocking reforms intended to end Somalia's "hopeless, bloody conflict" and eradicate militant and pirate groups seen as a growing menace to world security. REUTERS/Matt Dunham/POOL (BRITAIN - Tags: POLITICS)
Shugaban Somaliya Sharif Ahmed da Fira Minista Abdiweli Mohamed AliHoto: REUTERS

A karon farko cikin shekaru 20, yau Litinin ake ƙaddamar da sabuwar majalisar dokokin ƙasar Somaliya, a Mogadishu babban birnin ƙasar.

MDD ta ce sabbin 'yan majalisun za su samu kariya daga dakarun kiyaye zaman lafiya na ƙungiyar Tarayyar Afrika, inda ake gudanar da bikin a filin saukan jiragen sama na Mogadishu, da ke samun kariyar dakarun na kiyaye zaman lafiya.

Bayan zaɓen sabon kakakin majalisa, 'yan majalisu suna da aikin zaɓen sabon shugaban ƙasa, kuma ana saran Shugaba Sheikh Sharif Sheikh Ahmed, da ke kan madafun iko tun shekara ta 2009, zai iya lashe zaɓen, amma akwai wasu 'yan takara.

Akwai kimanin dakarun Tarayyar Afirka 17,000 da ke aikin tabbatar da zaman lafiya. Yau wa'adin gwamnatin da ke samun tallafin MDD ya kawo ƙarshe, kuma tunda fari, an zaci samun sabon Shugaban ƙasa, amma yanzu an bayyana tsaiko kan zaɓen sabon shugaban.

Mawallafi: Suleiman babayo
Edita: Yahouza Sadissou Madobi