'Yan Turkiya sun isa gida daga Iraƙi
September 20, 2014Talla
Turkawa 49 da Ƙungiyar IS ta kama a arewacin Iraƙi watanni uku da suka gabata, sun samu kuɓuta kuma sun isa gida lafiya kamar yadda Firaministan ƙasar ya ba da sanarwa.daga cikin mutanen da aka sace har'da wasu jami'an diflomasiyya da sojoji da yara ƙanana. A watan Juni ne dai aka sace mutanen cikin ƙaramin ofishin jakadancin Turkiya da ke Mosul. Gudun taɓa lafiyar mutanen ya hana Turkiya haɗa gwiwa a shirin Amirka na yaƙi da 'yan ta'addar wanda duniya ke shirin yi musu taron dangi.