1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Takun saka a siyasar Guinea Bissau

Suleiman Babayo USU
December 13, 2023

A birnin Bissau fadar gwamnatin kasar Guinea-Bissau 'yan sanda sun yi amfani da hayaki mai saka hawaye domin tarwatsa 'yan majalisar dokokin da aka rusa da suka yi yunkurin sake haduwa.

https://p.dw.com/p/4a7uE
'Yan sanda sun tarwatsa 'yan majalisar dokokin Guinea-Bissau da aka rusa da suka yi yunkurin sake haduwa
'Yan sanda sun tarwatsa 'yan majalisar dokokin Guinea-Bissau da aka rusa da suka yi yunkurin sake haduwaHoto: Alison Cabral/DW

'Yan sanda a birnin Bissau fadar gwamnatin kasar Guinea-Bissau sun watsa hayaki mai saka hawaye domin tarwatsa 'yan majalisa na bangaren adawa wadanda suka yi yunkurin haduwa duk da matakin Shugaba Umaro Sissoco Embalo na rusa majalisar.

A makon jiya shugaban kasar ya rusa majalisar wadda 'yan adawa suka mamaye, bayan wani yunkurin juyin mulki da aka yi inda aka samu harbe-harbe.

Karkashin dokokin kasar ta Guinea-Bissau da ke yankin yammacin Afirka, bangaren da yake da rinjaye a majslair dokoki yake nada jagororin gwamnati amma shugaban kasa yana da ikon rusa majalisar dokokin.